Arewa Plus
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Plus, Journalist, Kano.
30/03/2026
Yadda jiga-jigan ADC nakasa s**a yi wa Dr Rabiu Musa kwankwaso lale Marhaba da shiga jam'iyar ADC tare da dubban magoya bayansa kudu da arewa.
30/03/2026
Tsohon ministan sharia na Nigeria Abubakar malami SAN ya taya tsohon Gwamnan Kano Dr Rabiu Musa kwankwaso shigowa jam'iyar ADC
30/03/2026
Tsoron Dan takarar Gwamnan jahar jigawa a tutar jam'iyar NNPP a zaben 2023 ya bada sanarwar fitarsa daga jam'iyar NNPP ya shiga jam'iyar ADC.
26/02/2026
Ina yan kwankwasiya?
Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan bukatar samar da kwalejin Polytechnic a Gaya
19/10/2025
Hedkwatar Tsaro (DHQ) ta karyata wani rahoto da ke zargin cewa soke shirye-shiryen bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai wata makarkashiya ce da nufin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
trust
08/10/2025
Da dumi dumi: Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya ta ce an dakatar da aiwatar da binciken lasisin gilashin mota mai duhu bayan wani umarnin kotu da ya hana cigaba da wannan aiki.
01/10/2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta dakatar da Malam Lawan Triumph daga yon wa'azi
Majalisar Shura da gwamnatin Kano ta kafa ya sanar da dakatar da Malam Lawan Shuaibu Triumph daga yin wa'azi.
A wani taron manema labarai da Sakataren majalisar, Alhaji Shehu Wada Sagagi ya yi a yau Laraba, ya ce an dakatar da Malam Lawan ne domin bashi damar ya zo gaban majalisar ya kare kan sa daga zarge-zargen da ake yi masa na yin kalaman ɓatanci ga Ma'aiki.
A cewar Sagagi, an dakatar da Malam Lawan har sai an kammala bincike da jin ta bakin sa a matakin Majalisar ta shura.
Ya kuma yi kira ga ƴan siyasa da su guji tsoma baki a batun, inda ya bukaci da a kyale kwamitin ya kammala aikin sa.
Sagagi ya tabbatar da cewa Majalisar za ta yi aiki tsakani da Allah ba tare da don rai ko rashin adalci ba.
25/09/2025
Ana zargin matashi Mutawakkil, wanda aka fi sani da Tony, da kashe kakanninsa ta hanyar caka musu wuka a unguwar Kofar Ruwa da safiyar yau.
Rahotanni sun nuna cewa bayan kisan, matashin ya yi yunkurin tserewa ta shiga wani gida, amma al’ummar unguwar s**a yi ƙoƙarin cafke shi. Daga bisani jami’an Hisbah na Dala s**a iso wajen, s**a mika lamarin ga ’yan sanda, waɗanda s**a tabbatar da cafke shi tare da kai shi ofishinsu.
Kakannin nasa kuwa an garzaya da su asibiti domin duba lafiyarsu, sai dai daga bisani rundunar ’yan sanda ta Kano ta tabbatar da rasuwarsu.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce za a fitar da ƙarin bayani nan gaba.
Arewa plus
06/09/2025
Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kori dan majalisa mai wakiltar Kiru/Bebeji, Abdulmumini Jibrin Kofa daga jam’iyyar
02/08/2025
Da dumi dumi, al'ummar unguwar kofar mata dake cikin birnin Kano, suna gudanar da zanga zangar lumana, Saka makon fadan daba da ya addabe su.
This is 4tree fertilizer, for fermers hurry to grab your own at cheaper price
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the public figure
Website
Address
Kano