Jaridar Azurfa

Jaridar Azurfa

Share

Ingantattun labaran Afirka da duniya a tafin hannu! Babu sirki da soki burutsu

05/02/2026

WATA SABUWA: Ta Rabawa Manyan Hadimanta su 10 Naira Miliyan Daya kowannensu Domin Siyan Filaye a Zariya.

A wani mataki na nuna tsantsar kulawa, hangen nesa, da jajircewa wajen gina makomar Masu mata hidima, Fitacciyar mai Fafutukar tallafawa Mabukata da Marayu dake Zariya,Barrister Aysha Ahmad Mohammad (Addah) ta rabawa manyan yaranta guda goma 10 tallafin kuɗi har Naira Miliyan Daya 1,000,000,kowannensu wanda Jumla ya k**a Naira miliyan 10 domin su sayi filaye don tanadin gaba da cigaban rayuwarsu.

Wannan gagarumin tallafi ya zo ne a matsayin wani bangare na tsarin Addah Aysha na ƙarfafa yaranta domin su fara tanadi tun da wuri, tare da koya musu muhimmancin saka jari, mallakar kadarori, da dogaro da kai a nan gaba.

A cikin jawabinta, Addah Aysha ta bayyana cewa wannan mataki yana daga cikin burinta na ganin yaranta sun samu ginshikin rayuwa mai dorewa, tare da basu damar gina rayuwarsu bisa tsari mai kyau da hangen nesa.

“Ina son yarana su fahimci muhimmancin tanadi tun suna ƙuruciya. Mallakar fili ko gida yana daga cikin ginshikan tsaro da cigaban rayuwa, shi yasa na ga ya dace in tallafa musu tun yanzu,” in ji Addah Aysha.

Ta kara da cewa iyaye na da alhakin shirya ‘ya’yansu domin gobe, ba wai kawai ta hanyar ilimi ba, har ma da kayan more rayuwa da tsare-tsaren tattalin arziki da za su taimaka musu su dogara da kansu a nan gaba.

Cikin wadanda S**a Rabauta dun hada da Babban Mai Taimaka mata akan Kafofin Sadarwar Zamani Saifullahi Lawal Imam,da Babban Hadiminta kuma Direbanta Abbana H Abubakar,da P.A dinta Hajjo ,da Alamin Sunusi,da Fatima Hassan,Da Khady Suraj,sai Hajiya Uwale,Da Samira Abubakar da Jamilu Suleiman Bizara,wadanda dukkansu Manyan Hadimaine a Gareta.

Matakin Addah Aysha ya samu yabo daga al’umma da dama, inda ake kallonsa a matsayin abin koyi ga iyaye da shugabanni wajen kula da iyali da tsara makomar yara.

Masu sharhi sun bayyana cewa wannan tallafi ba kawai taimako ba ne, har ma darasi ne mai muhimmanci game da hangen nesa, jajircewa, da muhimmancin gina makoma tun daga yau.

02/02/2026

FILM DIN GIDAN DUNIYA..

Ya zamanto Film mafi Shahara da Kayatarwa a cikin Finafinan da aka taba yi a Kannywood,Saboda Tsaruwarsa da kyawunsa da Aikin da Aka masa.

Masana Sun Tabbata ba a tabayin Film mai Armashin Film din Gidan Duniya ba,inda s**a bayyanashi a matsayin mafi kyawun film a Duniyar Fina-finan Hausa.

Maza Ku hanzarta ku kalli shirin gidan Duniya, Episode 3 kai tsaye Yanzun haka a Youtube Channel Link na Comment Section.👇👇👇👇

24/11/2025

DA DUMI-DUMINSA: Uwargidan Shugaban Majalisar wakilai ta biyawa Mutane 2000 kudin aikin Ido a Zariya..

Maidakin Shugaban Majalisar wakilai ta Kasa Dokta Abbass Tajuddeen wato Hajiya Fatima Abbass Tajuddeen,ta dauki Nauyin Aikin ido kyauta ga marasa galihu mutum dubu biyu ciff a babban Asibitin koyarwa na A.B.U dake tudun wada Zariya. wanda tuni an shirya fara gudanar da aikin tantance wadanda za su ci moriyar aikin.

Uwargidan Kakakin Majalisar,wacce har wa yau ke rike da Saurautar Tauraruwar Iya,ta biya wannan gagarumin aikin ne karkashin Gidauniyarta ta Fatima Tajudeen Abbas inda daga gobe za a shirya shiri na musamman domin aiki ga masu lalurar Ido, da duk wani me fama da lalurar Ido,inda kwararru a fanni lafiyar ido zasu duba al'umma.

Bayan ga duba lafiyar idon, ga wanda idansu ke bukatan aiki nan take likitoci kwararru zasu masa aiki kyauta, haka ga wanda idan ke bukatan Tabarau (Eye Glasses) shima za a samar masa dai dai da yanda idansa ke bukata.

Wannan bashi ne karon farko ba da maidakin Shugaban Majalisar Wakilai ta Ƙasa Hajiya Fatima Abbas Tajudeen ke shirya irin wannan shiri domin kyautatawa Al'umma ba. watannin baya ta shirya gagarumin shirin koyar da sana'oi ga mata da matasa inda kowannensu ya rabauta da Jarin Naira Dubu Hamsin 50k.

Za a shafe kwanaki 5 ne dai ana tantance Mutane kafin fara gudanar da Aikin wanda shine irinsa na farko da za a duba dubunnan mutane kuma a musu aiki kyauta a Zariya. dama ce ga al'umman Zaria dama makofta akan su fito gobe ganin yanda harkan lafiyar ido tayi tsada, wannan shiri tinda ga farkonsa har karshe kyauta ne ba a bukatan komai daga mare lafiya.

Daga Saifullahi Lawal Imam.

18/05/2025

🚨🚨 Luka Modric ya shaidawa Real Madrid cewa a shirye yake ya rage albashinsa domin cigaba da zama a kungiyar a kakar wasa mai zuwa,

Jaridar Marca. 🤍🤜🏻

Wasu na ganin ya k**ata tsohon nan ya tashi ya bawa yara damar bugawa. Shi kuma ya nace.

09/05/2025

Kungiyar kwallon kafa ta arsenal. Sun iya buga tamaula cikin kwarewa. Amma babu wani abu da s**a rasa sai cin kofi kowanne iri ne!

A ganin ku menend wannan dalilin?

09/05/2025

Jumma'atu

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Kaduna?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Website

Address


Kaduna