Jewel Multimedia
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jewel Multimedia, Media/News Company, Gombe.
Jewel Multimedia Services
A modern media platform dedicated to telling stories that create impact through news, digital communication, and community development.
11/06/2026
Daliban Sashen Mass Communication na Jami'ar Tarayya da ke Kashere, karkashin ƙungiyar su ta MACOSA, sun gudanar da wani gagarumin gangami a harabar jami'ar a wani ɓangare na bukukuwan makon MACOSA na shekarar 2026.
Gangamin, wanda ya gudana ranar 10 ga watan Yunin 2026, ya samu halartar ɗalibai da dama waɗanda s**a fito cikin annashuwa domin nuna goyon baya ga bukukuwan ƙungiyar tare da wayar da kan al'ummar jami'ar game da ayyukan da ake gudanarwa a yayin makon.
Masu halartar gangamin sun zagaya sassa daban-daban na harabar jami'ar, inda s**a nuna haɗin kai da zumunci tsakanin ɗaliban Mass Communication tare da ƙarfafa sauran ɗalibai su shiga cikin shirye-shiryen da aka tanada.
An bayyana gangamin a matsayin mai cike da nishaɗi da armashi, lamarin da ya nuna jajircewar ɗaliban wajen tabbatar da nasarar bukukuwan MACOSA Week 2026.
Rahotanni sun ce taron ya gudana cikin lumana tare da nuna irin rawar da ƙungiyar ke takawa wajen ƙarfafa haɗin kai da bunƙasa harkokin ɗalibai a jami'ar.
✍️ Bashir Habeeb Adam
Media Director, MACOSA
25/12/2025
DA DUMI-DUMI: Ali Nuhu ya zama Ambasadan kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, bayan kulla yarjejeniyar Naira miliyan 30 na tsawon shekara guda
ABBA PANTAMI DATA LTD ya sake rage muku farashin Data zuwa Naira 500 akan kowane 1GB, ku hanzarta ku sauke Application din, domin ku more garabasa.
Duk wanda ya sayi Data mai 30DAYS a Application din ABBA PANTAMI DATA LTD to sai tayi kwanaki 30 sannan za tayi Expired. Akwai bambanci tsakanin Expired da kuma karewa.
Matukar kuna amfani da Application din ABBA PANTAMI DATA LTD da zaran ka hadu da matsalar network ko makalewar kudi kana yiwa customer care dinsu magana anan take zasu gyara maka.
Idan baka taba amfani da Application din ba ka gwada, idan ka dade baka yi amfani dashi ba ka sake gwadawa a yanzu domin tabbatar da ingancin shi.
Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore da kuma AppStore
👇👇
Ga link din PlayStore
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app
Ga link din AppStore
https://apps.apple.com/us/app/abba-pantami-data-ltd/id6744061271
Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000
Abba Sani Pantami
07061347599
05/12/2025
Jega Ya Gargadi Matasa Su Shiga Siyasa Ko Najeriya Ta Fuskanci Hatsarin Mulkin Danniya
Daga Muhammad Chigari Kumo
Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, ya yi kira mai ƙarfi ga matasan Najeriya da su ƙara shiga harkokin siyasa, yana jan hankalin cewa ƙasar na iya karkata zuwa mulkin danniya idan matasa ba su tashi tsaye ba.
Farfesa Jega ya yi wannan gargadi ne a jiya yayin gabatar da takarda mai taken “Zabe da Kyakkyawan Mulkin Dimokuraadiyya a Najeriya” a taron jawabin ilimi da Jami’ar Tarayya ta Kashere (F*K) ta shirya a dakin taronta na Multipurpose Hall.
Ya ce matsalolin mulki da Najeriya ke fuskanta a yau na da alaƙa kai tsaye da matasa, kasancewar su ne ginshikin cigaban kasa. Ya jaddada cewa rashin shiga harkokin siyasa da zabe na barin fagen siyasa a hannun mutanen da ke neman moriyar kansu maimakon cigaban kasa baki ɗaya.
A nasa jawabin, Babban Editan Premium Times, Dapo Olorunyomi, ya soki yadda ake gudanar da zaben fidda gwani ta hanyar kuɗi da kuma dogaro da kotuna wajen tantance sakamakon zabe. Ya ce irin wadannan dabi’u na rage amincewar jama’a ga tsarin dimokuraɗiyya, yana mai cewa babban kalubalen siyasar ƙasar shi ne tabbatar da cewa tsarin zabe yana amfanar da al’umma.
Mataimakin Shugaban Jami’ar Tarayya ta Kashere, Farfesa Umar Pate, wanda ya bude taron, ya bayyana shi a matsayin muhimmin mataki ga jami’ar da ƙasar, musamman a lokacin da ake neman sabunta dimokuraɗiyya da gina cibiyoyin gwamnati masu ƙarfi. Ya ce taken taron ya dace da halin da ƙasar ke ciki a yanzu.
Farfesa Pate ya kara da cewa jami’o’in gwamnati suna da muhimmiyar rawa wajen gina matasa masu ƙwarewa da kuma wayar da kan jama’a kan dimokuraɗiyya da shugabanci nagari.
Shugabannin jihohin Gombe da Taraba sun aika da sakonnin gaisuwa ta hannun Chiefs of Staff dinsu.
Tun kafin taron, Farfesa Jega ya ziyarci muhimman sassa na jami’ar, ciki har da Kwalejin Kimiyyar Likitanci, dakin gwaje-gwaje na zamani, sabbin dakunan karatu da aka gina, da Gidan Watsa Labarai na jami’ar.
02/12/2025
SRC Ta Raba Tallafi a Masaukan Daliban Jami’ar Tarayya Kashere
Majalisar Wakilan Dalibai ta Jami’ar Tarayya Kashere (SRC) ta gudanar da rabon tallafi ga daliban mazauna masaukan jami’ar, a wani mataki da aka bayyana a matsayin ci gaba wajen inganta walwalar ɗalibai da kyautata yanayin rayuwarsu. An gudanar da wannan aiki ne a ranar Litinin, 1 ga Disamba 2025.
A yayin bikin rabon kayan, Shugaban SRC, Kwamared Kabir Faizu Danyaya, ya ce wannan shiri na daga cikin ƙudurin majalisar na ganin cewa ɗalibai sun samu dukkan irin tallafi da kulawa da ya dace. Ya bayyana cewa SRC na ɗaukar walwalar ɗalibai a matsayin abin da ya fi komai muhimmanci a aikinsu na yau da kullum. Danyaya ya jaddada cewa taken su na “Ba a Bar Kowa a Baya” ya kasance mabudin ƙarfafa majalisar wajen ɗaukar matakai masu tasiri ga dalibai.
Shugaban sashen kwanan Dalibai, Dahiru Sulaiman Gwale, wanda ya karɓi kayan a madadin daliban masaukan, ya bayyana tallafin a matsayin wani abu da ya zo a daidai lokacin da ake buƙatarsa. Ya ce tsananin buƙatar kayayyakin tsafta da sauran kayan amfani na yau da kullum ya sa wannan tallafin ya zama abin jin daɗi ga dalibai, musamman duba da ƙalubalen da ake fuskanta a masaukan.
Wasu daga cikin daliban da s**a samu tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da jinjinawa majalisar bisa ga jajircewarta. Sun ce matakin na nuna cewa majalisar na bibiyar kalubalen da dalibai ke fuskanta tare da ɗaukar matakai kai tsaye ba tare da jinkiri ba.
Kayan da aka raba sun haɗa da robar ruwa, mujajjawa (moppers), tsintsiya, sabulai, Hypo da sauran muhimman kayan tsaftace muhalli kayan da ake amfani da su akai-akai wajen tabbatar da tsafta da ingantaccen yanayi a masaukan jami’ar.
Wannan shiri dai ya ƙara ƙarfafa gwiwar daliban cewa akwai ci gaba a aikace a tsakanin shugabannin majalisar, musamman wajen kula da buƙatun ɗalibai da kuma kawo sauƙi a rayuwar su.
02/11/2025
Ina Matafiya Wannan Hanyar A Wace Jiha Take A Nigeriya?
02/11/2025
DADUMI-DUMI: Yanzu Haka Matasan Karamar Hukumar Dukku Suna Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana Kan Lalacewar Hanyar Titin Gombe–Dukku–Darazo
A yau, matasa da dattawa daga ƙaramar hukumar Dukku da kewaye s**a fito kan tituna domin nuna damuwa kan halin da hanyar Gombe–Dukku–Darazo ke ciki, wadda ta dade tana cikin matsanancin lalacewa.
Hanyar, wacce ke da muhimmanci wajen haɗa jihohin Gombe, Adamawa da Bauchi, ta zama barazana ga rayukan jama’a saboda ramuka, rashin kyawunta, da yawan hatsari da ke faruwa a kullum.
Masu zanga-zangar sun gudanar da ita cikin lumana, ba tare da tashin hankali ba, inda s**a ɗauki banner na takardu masu rubuce-rubuce kamar:
- “Mu ma ‘yan Najeriya ne!”
- “Hanyar Gombe–Dukku tana kashe mu!”
- “Muna bukatar aikin gaggawa, ba alkawari ba!”
Wani daga cikin shugabannin zanga-zangar ya ce:
“Ba wai muna neman abun da bai dace ba ne; muna neman rayuka su tsira, tattalin arziki ya bunƙasa, da kuma a dawo da martabar wannan hanya wacce take jigon hulɗar kasuwanci da sufuri a Arewa maso Gabas.”
Sun kammala da kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su saurari ƙorafin jama’a, domin gyaran hanyar zai taimaka wajen tabbatar da tsaro, ci gaba, da haɗin kan al’umma.
24/10/2025
Sheikh Professor Isa Ali Pantami Ya Sa An Rushe Masallacin Kofar Hakimin Pantami, Zai Gina Sabon Masallaci Na Zamani
Babban malamin addinin Musulunci kuma tsohon Ministan Sadarwa na Najeriya, Sheikh Professor Isa Ali Ibrahim Pantami, CON (Majidadin Daular Usmaniyya), ya bayar da umarnin rushe tsohon Masallacin Kofar Hakimin Pantami da ke cikin garin Gombe, domin gina sabon masallacin Juma’a na zamani a wurin.
Rahotanni sun tabbatar da cewa, bayan rushewar masallacin, Sheikh Pantami ya sayi gidaje uku da ke gefen masallacin, domin fadada fili da samar da isasshen wurin ibada ga jama’ar da ke halartar sallar Juma’a.
A cewar mazauna yankin, wannan aiki na Sheikh Pantami ya zama abin yabo, ganin yadda tsohon masallacin ke da ƙaramin fili da kuma cunkoso, musamman a lokutan sallar Juma’a.
Wani daga cikin mazauna unguwar, Malam Abdullahi Haruna, ya bayyana cewa wannan mataki ya nuna irin kishin da Sheikh Pantami ke da shi ga addini da al’umma.
Sheikh Pantami mutum ne da ke nuna kishin addini da kulawa da jama’a. Wannan aiki da yake yi zai taimaka wajen kawo sauƙi da kwanciyar hankali ga masu ibada. Allah ya saka masa da alkhairi,” in ji shi.
Ana sa ran sabon masallacin da za a gina zai kasance na zamani, mai ɗauke da kayayyakin more rayuwa da tsarin da ya dace da zamani ciki har da na’urorin sanyaya iska, tsarin sauti na zamani.
Wannan aikin na cikin jerin ayyukan alkhairi da Sheikh Pantami ke gudanarwa a fadin ƙasar nan, musamman waɗanda s**a shafi gina masallatai, tallafawa malamai, da taimakon al’umma ta fannoni daban-daban.
A ƙarshe, jama’ar yankin sun roƙi Allah Ya saka wa Sheikh Pantami da alkhairi, tare da jinƙan iyayensa.
24/10/2025
HISBAH Pantami Yamma Ta Shayar Da Bayin Allah Ruwan Sanyi A Gombe
A yau Juma’a, rundunar Hisbah Pantami Yamma ta gudanar da wani aikin alkhairi mai matuƙar jan hankali na shayar da bayin Allah ruwan sanyi (pure water) a masallatai biyu a cikin birnin Gombe.
Aikin, wanda aka gudanar ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim M. Labaran, ya gudana ne a Masallacin Juma’a na Maizare (Ahajas) da kuma Masallacin Juma’a na Madina Quarters, Opposite Wuri Biriji, inda aka raba kwalaben ruwa ga masu halartar sallar Juma’a.
Rahotanni sun tabbatar da cewa mutum 660 ne s**a amfana da wannan shirin, wanda aka yi da nufin rage ƙishirwa da taimaka wa al’umma a wannan lokacin na zafi mai tsanani.
Da yake jawabi ga wakilanmu, Malam Ibrahim M. Labaran ya bayyana cewa wannan aiki wani ɓangare ne na shirye-shiryen Da’awah and Relief Organization Gombe wajen ganin an karfafa taimakon juna da ciyar da al’umma gaba.
Wannan ba kawai rabon ruwa ba ne, alkhairi ne da nufin ƙara haɗin kai da nuna kulawa ga bayin Allah. Muna fatan sauran ‘yan uwa musulmi za su yi koyi da irin wannan aiki, in ji shi.
A wasu wurare da aka kai ruwan, jama’a sun bayyana farin cikinsu da godiya ga rundunar Hisbah, inda s**a ce a wannan lokaci na zafi, ruwan sanyi ya zama wata ni’ima ta musamman.
Aikin ya kuma jawo yabo daga masu ibada da mazauna yankunan Maizare da Madina Quarters, inda aka yaba da yadda rundunar ke ci gaba da shirya ayyuka masu amfani ga al’umma.
Hakika, wannan shayarwa ta zama wata gagarumar nasara ga rundunar Hisbah Pantami Yamma, kuma ta zama abin koyi ga sauran kungiyoyi masu kishin al’umma a jihar Gombe.
#
Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Abdulrahman Kumo, Abdulrahaman Ahmad, Arki Ibrahim Samaila, Buharee Abdullahi Dam Roni, Adamu Ibrahim, Bello Muhammad Nuhu Masu, Garba Sa'idu Kumo, Sahabo Abdulkadir, Auwal Musa Gadawo, Mohammed Idris Mancy, Hassan Haruna Umar, Comrd Muazu Manga, Abdullahi Bello Kumo, Sadiq Abdallah Gombe, Abigail Kelmi Lazarus, Muhammad Dahiru, Àhmèd Sidi Lùggèrèwò, Sulaiman Salihu Annoor, Dg Kabir Usman, Shehu Ahmad Dukku, Hassan J Muhammad, Adamu Manjas, Passman Garba Muh'd Dalori, Usman Bello Tumu, Aminu Ahmad Pantami, Real Jay, Shehu Ali, Adamu Mohammed Danjuma, Tukur Abubakar Abuu Sadeeq, Prince M A Kumo, Abdulrashid Abdullahi Kano, Sadiq Ahmad, Babanladi Saro, Ibrahim Usman Gombe, Asheer Yusuff, Muhammad Ahmad Sheikh, Rabiu Saeedu, Shanawa Kanhawa Kumo, Muhammad Musa Muhammad, Abubakar Muhammad Bappah, Kabiru Yahaya Sambo-daji, Ahmed Saleh Ibrahim, Emmanuel Fatusi, Muhammad Kwairi Waziri, Muhammad Sani Ibrahim, Abubakar Mato Kumo
19/10/2025
LABARI MAI DADI
YANZU-YANZU: Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, ya rage muku farashin Data, kowa ya duba Application dinshi domin more garabasa.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Website
Address
Gombe
1238