Manara RADIO
Radio channel that sheds light to listeners in Africa,Middle East and across the globe, predominantly "HAUSA" on Islamic tenets and civilization
LABARUN DUNIYA
GWAMNATIN NAJERIYA NA KARA DAUKAR MATAKAN KARIYA DAGA CUTAR EBOLA
Gwamnatin Najeriya na kara daukar matakan hana shigowar cutar Ebola daga wasu kasashen Afurka da cutar ta bulla.
Cikin matakan har da kwamiti na musamman da shugaba Tinubu ya kafa don daukar matakan kariya daga cutar inda tuni shugaban ya ware Naira biliyan 10 don wannan aiki.
Shugaban ma’aikata na fadar A*o Rock Femi Gbajabiamila shi ne shugaban kwamitin inda masu ruwa da tsaki k**ar hukumar shige da fice, hukumar kula da filayen jirage da ma’aikatar cikin gida ke da wakilici.
Matakin karin azama ne ga cibiyar yaki da bazuwar cutuka NCDC don zuba ido kan duk fasinjoji masu shigowa Najeriya da duba yanayin jikinsu kafin wucewa cikin kasa.
An ba da umurnin zuba ido musamman ga jiragen Kenya, Ethiopia don cutar ta bayyana a kasar Dimokradiyyar Kongo da Uganda da ke makwabtaka da juna.
Hakanan za a ware sassa na killace duk wanda a ka samu da alamun cutar a filin saukar jiragen sama na Lagos da Abuja.
SHUGABA TINUBU YA JINJINAWA JAGORNACIN FIRAMINISTAN INDIYA NARENDRA MODI
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yabawa jagorancin firaministan Indiya Narendra Modi don yadda ya ke jagorantar daya daga fitattun kasashen Asiya na tsawon shekaru.
Modi dai a yanzu ya zama mafi samun damar tsawon jagoranci a tsakanin wadanda su ka rike kujerar firaminista a Indiya bayan samun nasarar zabe a wa’adi uku.
A sanarwa daga kakakin shugaba Tinubu Bayo Onanuga, shugaban ya ce hakika Modi ya karfafa dangantakar Najeriya da Indiya ta fannin diflomasiyya.
Bola Tinubu ya zayyana Modi a matsayin abokin Najeriya ya na mai taya shi murnar nasara a madadin dukkan ‘yan Najeriya.
Modi dai na daga shugabannin da ke rike da mukamin babban kwamanda na Najeriya wato CCON da ke zama lamba ta biyu mafi daraja bayan GCFR.
WATA GOBARA TA K**A WANI SASHEN NA MAJALISAR DATTAWAN NAJERIYA
An samu wata gobara da ta k**a wani sashe na dakunan tarukan majalisar dattawan Najeriya.
Gobarar ta taso ne bayan kammala zaman kwamitin hukumar kula da yankin Neja Delta inda ya tantance Zainab Marwa a matsayin memba ta hukumar mai wakiltar Arewa maso gabar.
An fahimci cewa wutar ta auku ne daga dakin cin abinci na dakin taro na 107 daga na’urar dumama abinci MICROWAVE da a ka bari ba tare da kula ba.
Wadanda su ka wajen sun yi gaggawar tafiya tudun tsira yayin da hayaki ya turnuka dakin kuma na samu shawo kan wutar gabanin fantsama zuwa wasu sassa.
An tabbatar ba a samu raunuka ba kuma ba a samu salwantar wata takarda ko wani abu ba a sanadiyyar gobarar.
A ALHAMIS DIN NAN MAJALISAR WAKILAN NAJERIYA ZA TA KADA KURI’A KAN RUNDUNAR ‘YAN SANDAN JIHA
A Alhamis din nan majalisar wakilan Najeriya za ta kada kuri’a don duba amincewa da gyaran dokar kafa rundunar ‘yan sandan jiha.
Mataimakin kakakin majalisar Ben Kalu da ‘yan majalisa 14 ke daukar nauyin kudurin kuma su ka nuna kwarin guiwar samun nasara.
An ruwaito Kalu na nuna ba mai dakatar da wannan kuduri kuma an yi hakan ne don inganta tsaro.
Masu daukar nauyin kudurin sun nuna kasa cimma nasarar dakile ‘yan ta’adda da sauran miyagun iri ya sa muhimmancin neman kafa rundunar ‘yan sanda ta matakin jihohi.
Gwamnatin shugaba Tinubu na mara baya ga kafa wannan runduna don karfafa harkokin tsaro daga yawan satar mutane da ta’addanci da ke ta’azzara.
IRAN TA AYYANA RUFE MASHIGAR RUWA TA HORMUZ
Kasar Iran ta ayyana rufe mashigar ruwan teku ta Hormuz mai muhimmanci ga sufurin danyen man fetur.
Wannan na zuwa ne bayan Amurka ta kai hare-hare cikin Iran da hakan ya illata yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran.
Tuni Iran ta ce ta kai farmaki bugun jiragen dakon mai biyu da su ka yi yunkurin wucewa ta mashigar.
Iran ta ce mashigar Hormuz za ta cigaba da kasancewa a rufe ruff har wani lokaci ta na mai gargadi kar kowace kasa a yankin ta sako jirgi ya nemi wucewa don zai fuskanci matakin farmaki.
Shugaba Trump dai dama ya yi alwashin kai farmaki mai zafi kan Iran da hakan kuwa ya kawo babbar tangarda ga tsagaita wuta.
LABARUN DUNIYA
GWAMNATIN OYO TA RUGUJE GIDAN BOYE WADANDA A KA SACE A BADUN
Gwamnatin jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya ta ruguje wani gida da barayin mutane ke adana wadanda su ka sace a babban birnin jihar Badun.
Wannan ya biyo bayan gano 'yar uwar tsohon ministar lantarki Adelabu da barayin su ka sace ranar 3 ga watan nan su ka ajiye su a gidan.
Akasin ya faro ne da sace Busayo John Paul a lokacin da ta ke kai 'ya'yanta tagwaye Peter da Paul makaranta a nan Badun din.
Ruguje ginin ya zo 'yan sa'o'i bayan kwamishinan 'yan sanda na jihar CP Abimbola Olugbenga ya zaga da manema labaru don duba ginin.
Kwamishina Olugbenga ya ce akwai mamaki yadda gidan da ke tsakiyar jama’a kuma mutane na ganin wadanda a ke satowa a kawo amma ba tare da kai rahoto ga hukuma ba.
Wadanda a ka sacen na cewa su na jin hada-hadar makwabtan gidan amma ba su iya fitowa ba.
Olugbenga ya bukaci jama’a su rika kai rahoton satar mutane ko wasu laifuka don daukar matakan da su ka dace.
GHANA TA DAWO DA 'YAN KASARTA 1000 DAGA AFURKA TA KUDU
Kasar Ghana ta yi nasarar dauko 'yan kasarta kimanin 1000 daga Afurka ta kudu inda a ke fama da kin jinin baki.
'Yan Afurka bakar fata na fama da hare-hare daga 'yan Afurka ta kudu kuma har hakan kan yi sanadiyyar mutuwa ko kisan gilla da asarar dukiya.
Ministan harkokin wajen Ghana Samuel Ablakwa ya fitar da sanarwar dawo da mutanen zuwa gida don kare su daga fitinar Afurka ta kudu.
An tanadi tsari na maraba da wadanda a ka dawo da su ta hanyar alkawuran sama mu su aiki kuma an raba mu su layukan waya da damar hawa yanar gizo don samun sadarwa da dangi da sauran abokan hulda.
Mutanen sun yabawa shugaban Ghana John Dramani Mahama don daukin da ya yi mu su.
Najeriya ma ta dau matakai ciki har da magana da hukumomin Afurka ta kudu su hukunta masu hannu wajen hare-haren kin jinin baki don ya zama matakin dakile mummunar dabi’ar.
ISRA’ILA DA IRAN SUN SHIGA SABON DAUKI BA DADI
Isra'ila da Iran sun shiga sabon dauki ba dadi da juna da hakan ke barazana ga wanzuwar shirin tsagaita wuta na Amurka.
Hare-hare da Isra’ila ke kai wa kan Lebanon da zummar gamawa da duk 'yan Hezbollah da Iran ke marawa baya ya haddasa daukar matakai daga Iran din.
An yi musayar hare-hare tsakanin kasashen biyu kuma an ga wajejen da Isra'ila ta kai wa farmaki a Tehran, Tabriz da Isfahan
Iran na bukatar a shigar da Lebanon a cikin yarjejeniyar tsagaita wuta ta na mai zargin Amurka da Isra’ila da keta yarjejeniyar.
Ba ma abun da ya fi zama damuwa irin hare-hare kan yankin Dahiyeh na kudancin Lebanon da kuma sassan tasoshin ruwa na Iran.
A nan alamu na nuna sai an samu jajircewa daga mai shiga tsakani wato Pakistan don wanzar da yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran.
SAUDIYYA MUSANTA HARI KAN FILIN JIRGIN SAMA NA YARIMA SULTAN
Saudiyya ta musanta wani rahoton hari kan filin jiragen sama na Yarima Sultan bin Abdul'aziz a yankin Alkharj.
Kakakin rundunar sojan Saudiyya Janar Turki Almaliki ya ce bayanan kai harin ba gaskiya ba ne.
An dai kunna jiniyar ankarar da mutane yiwuwar hatsari don harbo makami da a ka yi daga cikin Yaman amma makamin ya tsaya a hanya kuma harin bai yiwu yadda a ka tsara ba.
Hakika an daina samun hare-hare daga 'yan houthi a Yaman zuwa Saudiyya tun sulhun da a ka samu tsakanin Saudiyya da Iran zamanin shugabacin marigayi shugaban Iran Ebrahim Raisi da marigayi ministan wajen Iran Amir Hossein Abdollahian ya yi ta kai kawo har a ka dawo da dangantakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu.
Kasar Sin ta taka rawa wajen sulhunta Iran da Saudiyya amma hare-hare na Amurka da Isra'ila kan Iran sun sa mayar da hannun agogo baya.
LABARUN DUNIYA
MAJALISAR DATTAWA ZA TA DUBA MAFITA GA ‘YAN MAJALISAR 40 DA BA SU SAMU TIKITIN ZABE BA
Majalisar dattawan Najeriya ta bayyana aniyar duba mafita ga ‘yan majalisar 40 da ba su samu tikitin tsayawa zabe a zaben 2027 da ke tafe ba.
Shugaban majalisar Godswill Akpabio ya bayyana haka ga wadanda lamarin ya shafa kuma su ke cikin yanayin jiran tsammanin samun wata mafita bayan gudanar da zabukan fidda gwani a jihohinsu da wasu ke zargin gwamnoni sun yi babakere.
A wani lokaci a baya k**ar ‘yan majalisar sun samu albishir na cewa duk za su zarce in an zo babban zabe amma sai 40 a cikinsu su ka rasa damar.
‘Yan majalisar 40 da akasari daga jam’iyyar APC ne na cikin ‘yan majalisa 109 na majalisar dattawan.
Ba shakka an samu irin wannan bita ga wasu fitattu a majalisar a baya da su ka hada da shi kansa shugaban majalisar Godswill Akpabio da tsohon shugaban majalisar Ahmed Lawal.
Ba mamaki maslahar ta iya fitowa ta hanyar jam’iyya ko tattaunawa da gwamnonin da kuma yiwuwar tafiya kotu.
A na raderadin shugaba Tinubu ka iya sa baki ga wasu ‘yan jam’iyyar APC duba da irin gudummawar da su ka bayar ta goyon baya a majalisar ta 10.
BABBAR KOTUN TARAYYA TA YANKE HUKLUNCIN KISA GA WADANDA KE DA HANNU A HARIN OWO
Babbar kotun tarayyar Najeriya a Abuja ta yanke hukuncin kisa ga mutum 4 da ta samu da hannu a harin ta’addanci kan majami’ar katolika ta Owo a jihar Ondo a shekara ta 2022.
Harin dai na ta’addanci ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 41 da kuma raunata wasu mutum 140.
Mai shari’a Jostis Emeka Nwite ya yanke hukuncin bayan shari’ar da ta dau tsawon wata 8 kuma kisan zai gudana ta hanyar rataya.
Wadanda a ke samu da laifin an tabbatar na cikin kungiyar ta’addancin Alshabab da ke aiki a wajajen Kwara da Ondo.
Mutanen sun hada da Idris Abdulmalik Omeiza mai shekaru 25, Alqasim Idris mai shekaru 20, Jamiu Abdulmalik mai shekaru 26 sai Abdulhaleem Idris mai shekaru 25.
Duk da haka kotun ba ta samu mutum na cikon biyar mai suna Momoh Oyubo Abubakar mai shekaru 47 da laifi ba don haka ta wanke da sake shi.
JAM’IYYU 15 SUN SAMU MIKA SUNAYEN ‘YAN TAKARARSU GA INEC BISA KA’IDA
Jam’iyyu 15 sun samu nasarar mika sunayen ‘yan takararsu ga zaben shugaban Najeriya na 2027 kanm ka’idar lokacin da hukumar zabe ta gidaya wato zuwa 30 ga watan jiya.
Duk da an samu wani hukuncin kotu da ke buda damar har watan Satumba, amma jam’iyyu 15 sun samu nasarar mika sunayen da su ka hada da sanannu da kuma wadanda ba a saba jin sunayensu ba.
‘Yan takarar sun hada da na jam’iyyar da ke gado APC wato shugaba Bola Tinubu, sai a adawa ADC ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar yayin da sabuwar jam’iyyar adawa ta NDC ta tsayar da Peter Obi.
Wata takarar mai daukar hankali ita ce ta tsohon shugaba Goodluck Jonathan a PDP duk da an samu dan takarar bangare sai kuma Donald Duke a jam’iyyar PRP ta Malam Aminu Kano.
ISRA’ILA DA LEBANON SUN CIMMA WATA YARJEJENIYAR DAKATAR DA HARE-HARE
Isra’ila da Lebanon sun cimma yarjejeniyar dakatar da hare-hare biyo bayan zama karo na 4 da shiga tsakani na Amurka.
A nan sabuwar yarjejeniyar ta nuna Hezbollah za ta janye daga dukkan sassan kudancin Kogin Litani da ke dumfarar kan iyakar Isra’ila.
Kazalika a sassan tsaro na yankin an cimma amincewar sojojin gwamnatin Lebanon za su karbi dukkan matakan tsaro yayin da Hezbollah ta janye gaba daya.
Ba shakka dakatar da musayar wuta tsakanin Isra’ila da Hezbollah na daga sharuddan tsagaita wuta a yakin Iran da Amurka inda Iran ta ce lallai sai Isra’ila ta daina kai hare-hare kan Hezbollah in ba haka ba ba yarjejeniya tsakaninta da Amurka da ma Isra’ila.
Iran dai ke marawa Hezbollah baya inda ita kuma kungiyar ta Hezbollah ke tinkarar Isra’ila don hanata sakat matukar za ta cigaba da hare-hare kan Iran ko yankin Gaza.
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA JINJINAWA RUNDUNAR SOJAN RUWA YAYIN DA TA KE CIKA SHEKARA 70 DA KAFUWA
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa rundunar sojan ruwan Najeriya don aiki tukuru a yayin da ta ke bukin shekara 70 da kafuwa.
Wannan ya faru a taro da a ka gudanar a mashigar bakin ruwa ta EKO ATLANTIC a birnin Lagos.
Shugaban ya kuma kaddamar da jiragen ruwa uku don inganta ayyukan rundunar da su ka hada da NNS Olobiri, NNS Mambila da NNS Gurara.
Shugaba Tinubu ya ce hakika rundunar sojan ruwan Najeriya ta taka rawa wajen yaki da barayin man fetur na teku da ya ce hakan ya kara bunkasa hako danyen man fetur.
Kazalika shugaban ya ce rundunar ta yi kwazo wajen yaki da ta’addanci da ma yin su ba tare da izini ba.
Da ya ke jawabi shugaban rundunar sojan rowan Vice Admiral Idi Abbas ya ce sun samu nasarori a ‘yan shekarun nan da kulawar shugaban ga rundunar.
Idi Abbas ya yi amfani da damar wajen nanata mubaya’ar rundunar ga kundin tsarin mulki da kuma shuagban kasa.
‘YAN BINDIGA SUN YI KISAN GILLA GA KIMANIN MUTUM 8 A JIHAR FILATO
‘Yan bindiga sun yi kisan gilla ga kimanin mutum 8 da raunata wasu mutum 10 a yankin Barikin Ladi da ke jihar Filato.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun shigo yankin su na harbin kan mai uwa da wabi inda hakan ya tilasta mutane su ka arce don samun mafaka.
Mutanen dai da a ka kai wa hari na gudanar da taron murnar zagayowar ranar haihuwa ne BIRTH DAY a lokacin da maharan su ka shigo.
Kungiyar kare hakkin Dan’Adam ta AMNESTY ta yi Allah wadai da kisan gillar ta na mai dora alhakin hakan kan hukuma da matakanta ba su wadatar wajen kare rayukan jama’a ba.
Ba bakon abu ba ne samun hare-hare a jihar Filato da kan sa mutane zullumin samun harin ramuwar gayya ko ma aukawa fadan kabilanci ko ma na bambancin addini.
NDLEA TA CE MASU SHAN MIYAGUN KWAYOYI YANZU HAR DAFIN MACIJI SU KE AMFANI DA SHI
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA ta bayyana cewa yanzu mashaya miyagun kwayoyi sun kai ga amfani da dafin maciji don samun buguwa.
Daraktar wayar da kan jama’a na hukumar Shehu Muhammad Dankolo ya bayyana haka bayan kaddamar da gidan rediyo FM mai taken CLEAN BEAT na hukumar a Abuja.
Shehu Dankolo ya bayyana cewa masu shan miyagun kwayoyin kan yi dabarar aiki da abubuwan da ba sa cikin doka don samun maye k**ar dafin maciji, kashin kadangare, bunne bawali ya kwan biyu da sauran hanyoyi don kaucewa doka.
A nan Dankolo ya bukaci tsaurara dokokin hukunta masu shan miyagun kwayoyi don hakan zai taimaka wajen yaki da kwayoyin da kan haukata musamman matasa.
Dankolo ya ba da shawarar daina korar jami’an tsaro da a ka samu da aikata laifuka sanadiyyar shan miyagun kwayoyi don kar su kara tsunduma miyagun laifuka; kuma maimakon hakan a tura su cibiyoyin NDLEA na sauya tarbiyya don daidaita dabi’arsu.
TRUMP YA CE HAR YANZU AMURKA NA TATTAUNAWA DA IRAN DON SAMUN SULHU
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce har yanzu kasarsa na zantawa sosai da Iran don samun sulhun tsagaita yaki a yayin da Iran ta bayyana janyewa da duk wata yarjejeniya biyo bayan kutsawa can cikin Lebanon da Isra’ila ta yi.
Trump ya ce Iran ba ta sanar da Amurka cewa ta janye daga tattaunawa ba don haka duk tsawon lokacin tsagaita tattaunawar ba zai hana cimma buri ba.
Donald Trump ya ce a yi shiru ma a jira ya fi alheri don samun cimma yarjejeniyya, amma shirun ba ya nuna Amurka za ta kai farmaki kan Iran.
Duk da haka Trump ya ce kange tasoshin jiragen ruwa na Iran da Amurka ta yi na nan.
Iran dai ta nuna matukar takaici ga yadda Isra’ila ke aukawa Lebanon da sunan murkushe Hezbollah da hakan kan yi sanadiyyar kashe rayukan fararen hula da asarar dukiya.
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA BA DA TABBACIN CETO YARAN DA A KA SACE A OYO DA BORNO
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ba da tabbacin daukar duk matakan da su ka dace don ceto yaran da a ka sace a jihar Oyo da kuma Borno don dawo da su ga iyayensu.
Shugaban na magana ne a sakon da ya fitar don ranar yara ta duniya da ta zo daidai ranar da musulmi su ka gudanar da murnar idin babbar sallah.
Shugaban ya nuna damuwa yadda wasu yaran da a ka sace a jihar Oyo da Borno ba za su samu yin murnar da iyyaensu ba don haka ya yi amfani da sakon wajen ba da tabbacin matakan ceto dukkan yara da ke hannun miygaun iri.
Bola Tinubu ya kara da cewa ya ba da umurni baya ga ceto yaran a kuma kula da lafiyarsu da saita kwakwalwarsu don dawowa daidai daga yanayin firgici da su ka shiga.
Shugaba Tinubu ya gudanar da sallar idi ta babbar sallah a fadar Dodan da ke Lagos inda a ka ga mataimakinsa Kashim Shettima na Maiduguri wajen sallar idi da Shehun Borno Alhaji Garbai Umar Elkenemi.
DTTAIJON KASAR YARBAWA ALHAJI AJIBOLA YA CIKA SHEKARA 100 CIF A DUNIYA
Daya daga dattawan kasashen Yarbawa Alhaji Asahafa Ajibola ya cika shekara 100 cif a duniya a daidai ranar idin babbar sallah.
Shugaba Tinubu ya fitar da sako na musamman na taya murna ga Alhaji Ajibola a wannan tsawon rayuwa da ya samu a duniya ya na mai nuna jiran fitowar littafin tarihin dattijon.
A nan shugaba Tinubu ya zayyana Alhaji Ajibola a matsayin wanda ya gudanar da rayuwarsa da ta zama abin koyi ga jama’a.
Alhaji Ajibola wanda shi ne mahaifin shugabar hukumar kula da ‘yan Najeriya da ke ketare Abike Dabiri Erewa, ya yi ayyuka da su ka hada da a madaba’a ta kasa, hukumar hana fasakwabri da kuma kula da sashen sufurin jiragen sama na kamfanin hako man fetur na Shell.
Dattijo Ajibola na da ‘ya’ya, jikoki da tattaba kunne da a wannan labari ba a bayyana adadinsu ba don ba mamaki don taya murna ce ta tsawon rayuwa a ka yi ma sa.
DUK DA RASHIN AMINCEWAR AMAECHI DA HAYATUDDEEN, ADC TA AYYANA ATIKU A MATSAYIN DAN TAKARA NA ZABEN 2027
Duk da samun korafin nuna murdiya a zaben fidda gwani na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC daga tsohon gwamnan Ribas Rotimi Amaechi dad an kasuwa Muhammad Hayatuddeen, jam’iyyar ADC ta ayyana tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar a matsayin wanda ya lashe zaben.
Da wannan sak**ako, Atiku Abubakar Wazirin Adamawa zai sake samun damar takarar shugabancin Najeriya bayan gwadawa a baya musamman a inuwar PDP da AC.
Mai jagorantar tattara sak**akon Tunde Ogbeha, ya sanar da cewa Atiku ya samu fiye da kuri’a miliyan daya da dubu dari takwas ya ya nasara kan Amaechi da ya samu kuri’a sama da 500 da kuma Hayatuddeen da ya samu wajen dubu 177.
An fara tattara sak**akon tun daga jihohi har a ka kammala a babban otel din nan na Tarnscorp a Abuja.
Atiku ya lashe zaben a akasarin jihohin Arewa da nasara mai yawa inda shi ma Amaechi ya taka rawa a yankinsa na kudu maso kudu.
RUNDUNAR SOJAN IRAN TA CE BA TA JIN ZA A DAWO GWABZAWA DA AMURKA
Rundunar sojan kasar Iran IRG ta ce ba ta tsammanin za a dawo gwabza yaki tsakanin Iran din da Amurka ko Isra’ila yayin da a ke neman daidaitawa kan sharuddan tsagaita yaki gaba daya.
Wannan ya biyo bayan hare-hare da Amurka ta kai cikin Iran a sassan kera mak**ai masu linzami duk da tsagaita wuta da a ke ciki.
Jami’in rundunar Muhammad Akbarzadeh ya ce akwai alamun abokan hamayyarsu na yakin sun samu rauni don haka ba za su so dawo da yakin ba.
Tamkar an shiga wani babin yakin caccar baki da farafaganda tsakanin sassan biyu tun bayan fara wannan yaki a watan Febrairu.
Kasar Pakistan na jagorantar shiga tsakani don dakatar da yakin amma har yanzu ba a cimma matsaya kan bude mashigar ruwar Hormuz da batun kera mak**an kare dangi na Iran ba.
Har yanzu ba za a iya cewa ga bangaren da ya samu galaba a wannan yakin ba musamman don rashin nasarar cimma burin Amurka na kifar da gwamnatin Tehran.
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA YI ALWASHIN AYYUKAN RAYA TATTALIN ARZIKI DA MASANA"ANTU IN YA ZARCE
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi alwashin dagewa kan ayyukan raya tattalin arziki da masana'antu in ya zarce a zaben 2027.
Bayan tabbatar ma sa lashe zaben fidda gwani na jam'iyyarsa ta APC don shiga babban zaben, shugaban ya ce karin wa'adin shekaru 4 sabuwar dama ce ta bunkasa tattalin arziki da zamantakewa a Najeriya.
Shugaban ya godewa jami'an jam'iyyarsa APC wajen shirya zaben fidda gwanin cikin nasara.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya Anyim Pious Anyim ne ya jagoranci zaben da kuma masu tattara sak**akon a Abuja da akasari gwamnoni ne.
Shugaban APC Nantawe Yilwatda ne ya mikawa shugaba Tinubu tikitin shiga zaben tazarce a Taron da a ka gudanar a babban dakin taro na kasa da kasa a Abuja INTERNATIONAL CONFERENCE CENTER.
Shugaba Tinubu ya samu kimanin kuri'a miliyan 11 inda dan takarar da ya kalubalance shi Stanley Osifo ya samu kuri'a dubu 16.
Bai zama wani abun mamaki ba shugaban da ke gado ya lashe zaben fidda gwani da hamayya ko ba hamayya don muradun siyasar jam'iyya.
RUNDUNAR SOJAN NAJERIYA TA TURA DAKARU BENIN A WATAN JIYA
Rundunar sojan kasar Najeriya ta tura dakaru a bataliya zuwa jamhuriyar Benin a watan jiya don ba da kariya lokacin zaben shugaban kasar.
Kakakin rundunar Misis Kanar Appolonia Anele ta ce dakarun ba su sa baki a harkar zaben ba amma sun tsaya a muhimman sassa don tabbatar da tsaro a ciki da wajen babban birnin kasar Kotono.
Dakarun sun tsaya a Benin har mika mulki ga sabon shugaban kasar Romuald Wadagni don muradun kare dimokradiyya ta tsarin kungiyar raya tattalin arzikin Afurka ta yamma ECOWAS.
Zai yiwu sojojin da su ka shiga Benin sun kai kimanin 150 kuma sun samu yabo daga babban hafsan sojan kasan Najeriya Waidi Shuaibu.
A bara ma shugaba Tinubu ya ba da umurnin tura dakaru zuwa Benin don kwatar da yunkurin juyin mulki ga tsohon shugaban kasar Patrice Tallon.
AN RUWAITO DANGOTE DA SHIGAR DA KARA DON HANA NNPCL BA DA LASISI GA FATAKEN FETUR
An ruwaito cewa dan kasuwa Aliko Dangote ya nufi kotu don bukatar ta dakatar da kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL daga ba da lasisi ga fataken shigo da tataccen man fetur.
Rahoton ya bayyana cewa Dangote na ganin ba da irin wannan lasisi zai yi karantsaye ga matatar fetur dinsa da ke Lagos wacce ya ce ta iya kenan wadatar da Najeriya da man.
Aliko Dangote na daukar wannan yunkurin na NNPCL da rashin yabawa kokarin da ya ke yI na wadata kasa da fetur kuma daga matatar da ke cikin Najeriya.
Wato a nan Dangote na ganin ya dace 'yan Najeriya su yi alfahari da matatar maimakon biyewa masu shigo da hajar daga ketare.
A nan akwai zargin ba lallai matatar Dangote ta iya wadata Najeriya da fetur ba kuma musamman kan farashi mai rahusa.
Hakanan wasu ma na zargin hatta Dangoten na hadawa da kasuwancin shigo da mai daga ketare.
YAU TAKE RANAR ARFA TA HIJRA 1447
Yau Talata 26 05 2026 ce ranar hawa ARFA ta hijra 1447 inda alhazai daga Makkah za su wuni a filin ARFA k**ar yadda ya ke a ka'idar aikin hajji.
Alhazan daga fadin duniya na barin tantunan Muna a daf da Makkah don isa filin na ARFA da ke zama cikin rukunan aikin hajji.
Limamin masallacin Madina Sheikh Abdallah Khuzaifi ne zai gabatar da hudubar ARFA a masallacin Nameera da ke yankin filin arfa.
Bayan kammala hawa ARFA alhazai za su taho Muzdalifah su kwana a fili kafin wucewa wajen jifar Shaidan.
Musulmi da ba su samu zuwa hajji ba kan yi azumi a ranar ta ARFA don samun falala mai tsoka.
Larabar nan 27 ga watan nan na Mayu ta ke ranar idin babbar sallah.
LABARUN DUNIYA
HUKUMAR YAKI DA BAZUWAR CUTUKA TA NAJERIYA NCDC TA CE SAM BA EBOLA A NAJERIYA
Hukumar yaki da bazuwar cutuka ta Najeriya NCDC ta ce sam ba yaduwar muguwar cutar nan ta EBOLA a duk fadin Najeriya.
Yanzu haka hukumomin lafiya sun dau matakai a filayen jiragen sama na tantance masu zirga-zirga zuwa Najeriya yayin da cutar ta EBOLA ta bayyana a jamhuriyar dimokradiyyar Kongo da Uganda.
NCDC ta fito da sanarwar don yadda wasu ke yayata cewa cutar ta iso Najeriya alhali hakan ba gaskiya ba ne.
Hukumar ta NCDC ta nuna illar yayata jita-jita kan irin wannan cuta mai kisa da irin haka a shekarun baya ya haddasa rasa rayuka don yadda wasu mutane su ka rika sha da wanka da rowan gishiri a matsayin rigakafin cutar.
Hakanan NCDC ta bambanta cutar EBOLA da HANTA VIRUS wacce ke yauduwa ta hanyar shakar kurar da ke kunshe da bayan gidan ‘yan dabbobi masu buruntu, inda EBOLA kuma sai mutum ya hadu da jiki ko gumin mai cutar.
FUBARA YA JANYE DAGA TAKARAR TIKITIN TAZARCE NA GWAMNAN RIBAS A APC
Gwamnan jihar Ribas Siminalayi Fubara ya ayyana janye takarar zaben fidda gwani na tikitin gwamnan jihar Ribas.
Fubara ya ce ya yi hakan ne don muradun zaman lafiyar jihar ta Ribas, ya na mai cewa zaman lafiyar Ribas ya fi muradun kowa.
Duk da janyewar, Fubara ya godewa shugaba Tinubu kan goyon bayan da ya ce ya samu a tafiyarsa ta siyasa ya na mai zayyana APC a matsayin jam’iyyarsu.
Gudun kar a yi ma sa fassarar raurawa ko tsoro, Fubara ya ce ba fargaba ta sa shi saranda ba sai da ya yi tuntuba, kuma ya ba wa magoya bayansa hakuri don ya san zafin da za su ji.
An fahimci cewa APC ta ba ta tantance magoya bayan Fubara a muk**an da su ke nema na majalisa ba, amma magoya bayan ministan Abuja Nyesom Wike sun tsallake.
Ba mamaki ta yiwu ko Fubara ya tsaya ba zai samu tikitin ba don haka da muguwar rawa gwara kin tashi.
MATAIMAKIN SHUGABAN NAJERIYA KASHIN SHETTIMA YA CE WASU SUN KULLA MA SA SHARRIN NEMAN CUTAR DA SHUGABAN KASA DA WASU TUFAFI
Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya bayyana cewa wasu mutane daga jiharsa ta Borno sun zo sun tseguntawa shugaba Tinubu cewa ya kulla cutar da shi don karbe mulki daga wasu tufafi da ya ba shi a kamfen din 2023.
Shettima ya ce tsegumin ya zo ne watanni 3 bayan fara mulkinsu biyo bayan shan rantsuwa a ranar 29 ga Mayu 2023.
Kashim Shettima na magana ne a taron kaddamar da littafi na tarihin aiki na tsohon shugaban mulkin soja Janar Yakubu Gowon a Abuja.
Shettima ya ce shugaba Tinubu ya sanar da shi labarin inda ya kuma cigaba da sanya kayan don bai amince da tsegumin ba.
Mataimakin shugaban kasar ya nuna damuwa cewa hakan samuwar rashin amana ce da ta shigo harkar siyasar Najeriya.
Hakika an yi ta samun jita-jita kan tunanin samun Baraka tsakanin shugaba Tinubu da Shettima har ma a na tunanin zai yi wuya Tinubu ya sake daukar Shettima a mataimaki a takarar zaben neman tazarce.
SAUDIYYA TA YABAWA TRUMP DA BIN MATAKAN DIFLOMASIYYA MAIMAKON SAKE FARMAKI KAN IRAN
Saudiyya ta yabawa shugaban Amurka Donald Trump don yadda ya zabi bin tattaunawar diflomasiyya maimakon cika bazaranar da ya yi ta kai hari mai zafi Iran a ranar Talata da ta wuce.
Ministan wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan ya isar da wannan yabo da Saudiyya ke ganin abun maraba ne.
Bin Farhan ya ce akwai bukatar Iran ta yi amfani da damar wajen samun sulhu da zai tsayar da wannan yaki.
Ministan ya nuna kwarin guiwa matakin ka iya kawo maslaha da ma bude mashigar ruwan teku ta Hormuz don safarar man fetur salun-alun
Iran a yanzu haka na nazartar sharuddan tsagaita yakin da Amurka da kuma Isra’ila don samun matsayar da za ta kwantar da fitinar.
Hakika Iran ta nuna jajircewa a yakin da har ya kai wannan tsawon musamman ba tare da faduwar gwamnatin Tehran ba.
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA NUNA JUYAYIN LABARIN KISAN GILLA GA DAYA DAGA MALAMAI DA A KA SACE A JIHAR OYO
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nuna matukar juyayin labarin kisan gilla ga daya daga malaman da a ka sace a makarantar Grammar ta Baptist da ke karamar hukumar Orire a jihar Oyo.
Rahotanni sun bayyana masu satar mutane sun sace malamai da daliban a makarantar ta al’ummar Esiele a karamar hukumar Orire.
Shugaba Tinubu ya ce babban sufeton ‘yan sanda na jagorantar ceto wadanda a ka sace, inda ya yi amfani da sakon wajen jajantawa gwamna Seyi Makinde da al’ummar Oyo kan wannan akasin.
Kazalika shugaba Tinubu ya nuna wannan na nuna lokaci ya yi da za a kafa rundunar ‘yan sandan jiha.
Shugaban ya bukaci majalisar dokoki ta gaggauta yin doka don kafa rundunar ‘yan sandan jiha da hakan zai taimaka wajen kula da yankunan da ba su da wadatar jami’an tsaro.
Yayin da gwamnatin tarayya da gwamnoni da dama ke mara baya ga kafa rundunar ‘yan sandan jiha, wasu masu sharhi na nuna fargaba ‘yan siyasa ka iya juya lamarin ‘yan sandan zuwa ‘yan kanzaginsu.
RUNDUNAR SOJAN NAJERIYA DA HADIN GUIWAR AMURKA SUN KAI FARMAKI KAN ‘YAN ISWAP
Rundunar sojan Najeriya da hadin guiwar rundunar sojan Amurka ta Afurka sun kai farmaki ta samaniya kan ‘yan ta’addan ISWAP a yankin Arewa maso gabashin Najeriya.
Hare-haren k**ar yadda sanarwa daga daraktan labaru na rundunar tsaron Najeriya Manjo Janar Samaila Uba ta bayyana cewa farmakin ya hallaka jigogin ta’addan ISWAP 20.
A cikin harin dai har da labarin kashe kwamandan ISWAP Abu Bilal Al-Manuki wanda ba mamaki wani mai k**a da sunansa ne a ka ba da rahoton kashewa a can baya.
Manjo Janar Uba ya ba da tabbacin cigaba da hare-hare don kore duk ‘yan ta’adda su rasa mafaka a yankin kasar Najeriya.
In za a tuna rundunar sojan Najeriya ko gwamnatin Najeriya ta ba da labarin hadin guiwa da sojan Amurka inda akalla sojojin Amurka 100 su ka sauka a Najeriya ta birnin Bauchi.
TSOHON GWAMNA ELRUFAI YA KI FITA DAGA MOTA LOKACIN DA A KA GARZAYA DA SHI OFISHIN DSS
Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasiru Elrufai ya ki amincewa ya fito daga mota lokacin da a ka garzaya da shi ofishin rundunar tsaron farin kaya DSS.
Wannan dai ya biyo bayan samun beli da ya yi amma da sharudda masu tsauri da su ka hada da mika fasfo dinsa da kuma zuwa kai kansa ofishin DSS duk Jumma’a har a kammala shari’a.
Nasiru Elrufai dai ya tsaya lallai sai a maida shi ofishin hukumar yaki da cin hanci ta ICPC inda ya ke tsare a halin yanzu.
Alamu na nuna Elrufai na fargabar shiga wajen tsaro na DSS don zai zama waje mafi tsauri na iya ganawa da jama’a ko ma kai ma sa abinci.
Iyalan Elrufai na zargin hukumar ICPC na kawo cikas wajen kai wa maigidan nasu abinci inda ICPC ta musanta hakan.
Yanzu dai za a jira a ga yiwuwar cika sharadi don nasarar belin Elrufai, kasancewar kotu ta nuna matukar ya saba ka’idar belin za ta soke izinin ko hurumin kai tsaye.
Elrufai daga jam’iyyar adawa ta ADC, ya shiga karin tsaka mai wuya a wata zantawa inda ya nuna ya na sauraron bayanan sirri na ofishin mai ba da shawara kan tsaro Malam Nuhu Ribadu.
SHUGABAN LEBANON AOUN YA CE ZAI YI ABUN AL’AJABI WAJEN DAKATAR DA YAKI DA ISRA’ILA
Shugaban Lebanon Mr.Joesph Aoun ya ce zai dau mataki mai ban mamaki ko ma marar yiwuwa a tunani don kawo karshen yaki da Isra’ila ke kawowa kan Lebanon.
Aoun ya bayyana haka ne bayan samun tattaunawar kai tsaye da Isra’ila amma hakan bai dakatar da hare-haren Isra’ila ba.
Tun samun yarjejeniyar tsagaita wuta a 17 ga watan Afrilu, Isra’ila ta cigaba da kai farmaki kan kudancin Lebaon da sunan murkushe ‘yan Hezbollah da Iran ke marawa baya.
Isra’ila har ta kan ba da wa’adi ga matsugunai a kudancin Lebanon su tashi don shirin kai farmaki.
Hezbollah ma ta ce ba ta ja da baya ba, don ta kai harin jirgi marar matuki kan wata cibiyar tsaron sojan Isra’ila a Arewacin Isra’ilar.
Zuwa yanzu daga fara wannan yaki, Isra’ila ta yi sanadiyyar kashe fiye da mutum 2,900 da jikkata wasu mutane ciki kuwa da kashe mutum 400 tun samun yarjejeniyar sulhu.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Telephone
Address
Utako District
Abuja