Hadejia Emirate Youth Forum

Hadejia Emirate Youth Forum

Share

...in God (alone) I seek refuge UNITED WE STAND!

Guri, Kirikasaamma, Birniwa, Malammadori, Kaugama, Auyo, Kafin Hausa duk Hadejiwane, "tsintsiya madaurinki daya"

Founder
Comrade Muhammad Babangida Muhammad
08064822229, 07052799752
[email protected]
[email protected]

Photos from Hadejia Emirate Youth Forum's post 22/10/2024

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UUN.

GASKIYA MUNA CIN CITTA A ƘASAR NAN. ALLAH YA KAWO MANA SAUƘI.

A zangon farko na shekarar 2023, da kuɗi NAIRA MILIYAN ƊAYA ina sayen buhunan CITTA guda hamsin daga kasuwar Kurmi Kano zuwa Haɗejia, duk mako ina sayarda kamar buhu 100 akan N22,000. Idan aka kawo mini buhunan cittar nan aka jibge mini su a ƙofar shagona kowa yazo shigewa sai ya sake duba kayan nan, ni kaina har wani ƙarfi nake ji a jikina, saboda ina da ƙarfin jari, kuma Alhamdulillah, ana samun ribar Dubu ɗaya zuwa Dubu ɗaya da rabi a kowane buhu duk mako.

A halin yanzu wannan Naira MILIYAN ƊAYAN buhu 3 kacal zata iya saya mini sai a bani chanjin da bai shige Naira Dubu goma ba wanda da su za a biya kuɗin mota da na dako daga kasuwar Kurmi zuwa Haɗejia.

Ku duba bambancin giɓin da kyau kuma da idon basira, Daga buhu 50 zuwa buhu 3 kacal Kuma a kuɗi ɗaya, Subhanalillahi 😭😭😭

A wancan lokacin ɗankoli ɗaya yana sayen buhu 3, 4, 5 har zuwa 10, Amma a yanzu ba wanda yake iya sayen koda rabin buhu, sai dai kwano ɗaya zuwa biyu ga masu ƙarfi kenan a cikin masu sana'ar mu ta KOLI.

Ƙananan ƴan kasuwa da yawa sun karye, sakamakon matsananciyar tsada ta sanya suna yin CINIKI-ƁATAR. Gaskiya ƙananan ƴan kasuwa suna cikin halin ni -ƴasu ga ƙarancin taimako a tsakaninmu, sakamakon kowa-ta-kansa-yake.

CITTA dai ba abinci ba ce, amma SINADARI ce mai inganta ɗanɗanon abinci, sannan kuma ana Sanya ta a magunguna da yawa.

Muna addu'ar Allah ya kawo mana sauƙin wannan tsanani Na tsadar rayuwa, amin.

13/02/2024

Yadda aka yi hada-hadar kudaden waje zuwa Naira a kasuwar sauyin kudi ta Wapa da ke jihar Kano.

07/10/2022

002
ZALUNCIN HUKUMAR RAYA FADAMUN KOGUNAN HADEJIA- JAMA'ARE

YUNKURIN NEMAN HAKKI.

KURA DA SHAN BUGU, GARDI DA AMSHE ABINCI.

Halin da manoman Kasar Hadejia da kuma al'ummar da ke da mazauni a ga6ar Kogin Hadejia suke ciki kenan. Hukumar (HJRVDA) ce da ke da alhakin tattara ruwan da adana shi da kuma rabawa don amfanin manoma musamman a lokacin aikin RANI. Wannan Hukuma ce ke da alhakin YASHE KOGUNAN don ruwan ya samu saukin shigewa zuwa Jihar Yobe, Borno da wani yanki na KAMARU da CHADI, amma ta gaza yin hakan a shekaru da dama da s**a shude, alhali tana da ikon sakin ruwan don amfanin manoma, amma abun takaici manoma da yawa sun dogara da tona rijiya da sayen INJI da man FETUR ko DIESEL don shayar da gonakin su. Hakan yana faruwa a muhallin da Hukumar take bayarwa haya don ayi noman, amma don tsabar mugunta ba zasu saki ruwan ba sun karkata don amfanin wata Jihar na samun hasken lantarki, wanda ba hakane ainihin dalilin yin MADATSAR RUWAN ba.

Babu hujja a ajiye ruwan da yakamata a sakar mana muyi amfani da shi a lokacin da muke bukata amma sai a hana kuma a sako shi a lokacin da bamu bukatar sa yana haifar mana asarar RAYUKA, MUHALLI da kuma GONAKI.

Bai kyautu mu zuba ido irin wannan 6arna tana faruwa duk shekara ba. Ana tauye TATTALIN ARZUKIN mu ne ta yin hasarar rayuka, muhalli, gonaki da kuma dabbobi.
Ku tashi mu farka HADEJIAWA mu KALUBALANCI aiyukan wannan HUKUMA na zalunchi da take aiwatarwa a muhallin mu.

Wani abun lura shine inda ake TATTARA RUWAN baya musu BARNA sai MU da muke bukatar sa a lokacin aikin RANI ake hana mu, kuma a sake shi lokacin da bamu bukatar sa.

A karshe muna sake sanar da yan uwa MANOMA musamman na KASAR HADEJIA cewa muna ci gaba da tattara bayanai akan yawan asarar da muka yi don GURFANAR da wannan HUKUMA gaban KULIYA MANTA SABO.

Dr Isah Billami Hadejia ,
Manomi, Dan kasuwa,
Mai gwagwarmayar neman hakkin al'umma.

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Hadejia?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Telephone

Website

Address

Hadejia